Mutane uku da ba a rubuta musu zunubi ko da sun aikata
Akwai mutane guda uku Wadanda an dauke alkalami a Kan su Ma'ana ko da sun aikata zunubi Allah bazai kama su da laifin zunubin ba
Sanin kowa ne Allah ya tabbatar Mana da cewa akwai mala'ikun da suke rubuta aiyukan da kowa ya keyi Amma su wadannan mutane uku baza a rubuta musu zunubi ba a yayin da suka aikata shi
Ko wanne daga cikin su an dauke mishi alkalamin ne saboda dalili ce ya kama Kuma a cikin wannan rubutun Zan baiyana dalilin na ko wanne daga cikin su
Ga jerin mutanen da a Ka dauke musu alkalami
Wadanda a ka dauke Alkalami a Kan su sune kamar haka;
1. Karamin yaro
2. Mahaukaci
3. Wanda yake Bacci
Karamin Yaro: An dauke Alkalami a Kan karamin Yaro Wanda bai balaga ba har sai lokacin da ya balaga ne za a fara rubuta mishi zunubai da yake aikatawa a Littafin shi
Mahaukaci; Na biyu daga cikin mutanen da a ka dauke musu alkalami shine mahaukaci, duk zunubi da mahaukaci yake aikatawa ba a rubutawa sai Idan Allah ya kaddari warkewan shi.
Idan ya warke daga Nan ne za a fara rubutu a littaLit shi na ko wane irin aiki da yake aikatawa.
Karanta: Yadda zaka sayi 200mb a kan Naira 50 a layin MTN
Wanda Yake Bacci: duk mutumin da yake Bacci shima an dauke alkaAlka a Kan shi, ko da lokacin Sallah zai yi har ya wuce Bai yi ba, da yake Bacci ya keyi ba zai iya sanin lokacin ibada yayi ba don Haka a ka dauke mishi alkalami har sai ya farka.
Wadannan sune mutane uku da aka dauke Alkalami a Kan su
Kayi like na shafin mu na Facebook a Nan
Asagist Facebook Page don ganin sabbin rubutun mu na gaba.
Kayi subscribes na blog din mu da email din ka don samun sabbin rubuce-tubucen mu ta akwatin email din ka.

Comments
Post a Comment